Dan takarar neman Gwamna a jam’iyyar APC Sanata Kabiru Marafa yana zargin Gwamnan Jihar Zamfara Abdul’aziz Yari da horar da matasa dubu 8,500 a matsayin jami’an tsaron farin kaya na JTF da nufin amfani da su wajen gudanar da harkokin zaben 2019 a jihar.
A cewar Gwamna Yari, ya sanar da horar da matasan ne don tabbatar da zaman lafiya a jihar tare da magance kalubalen tsaron da ke addaban jihar.