Shugaba Muhammadu Buhari tare da Mataimakinsa Yemi Osinbajo suna shirin shan rantsuwa a dandalin Eagle Square a yau Laraba.
Yayin da ake shirin rantsar da Gwamnoni 29. Majiyarmu ta samu rahoton cewa, wasu Gwamnonin masu barin gado tun kafin yau sun mika bayanan ayyukan da suka yi ga sababbin Gwamnonin da zasu dauki ragamar jihohin.