A yau Litinin Majalisar Dattawa zata ci gaba tantance sunayen Ministoci da Shugaba Buhari ya aika wa Majalisar, Ministocin da za a tantance su su tara sun hada da: Sanata Gbemisola Saraki (Kwara), Babatunde Fasola (Lagos), Rauf Aregbesola (Osun) da Geoffrey Onyema (Enugu).
Sauran sun hada da: Maryam Katagum (Bauchi), Mohammed Mahmoud (Kaduna), Suleiman Adamu (Jigawa) da Goddy Jeddy-Agba (Cross River) da Clement Agba (Edo).