A yau Litinin ne ake ci gaba da sauraran karar da ake yi wa tsohon Gwamnan jihar Katsina Ibrahim Shema tsakanin gwamnatin jiha da gwamnatin tarayya a babbar kotun jihar Katsina.
Kotun dai na tuhumar Shema ne akan zambar kudade da suka kai adadin naira biliyan 17.
Hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa ta’annati ta Najeriya, EFCC ce ta kai tsohon Gwamna Shema tare da wasu mutum uku da suka hada da: Sani Makana da Ibrahim Yankaba da Lawal Safana zuwa babbar kotun akan laifin karkatar da kudin da suka kai naira biliyan 11 na kananan hukumomin jihar.