Gwamnan Jihar Zamfara, Abdulaziz Yari ya zabi Kwamishinan Kudin Jihar Zamfara, Mukhat Idris Kogunan Gusau a matsayin wanda zai gaje shi.
Kwanakin baya Aminiya ta ruwaito cewa Mataimakin Gwamnan Ibrahim Wakkala ne zai tsaya takarar gwamnan, sannan shi kuma gwamnan na yanzu zai tsaya takarar sanata, a wata irin yarjejeniya da ake tunanin an kulla tsakanin tsohon Gwamnan Jihar Yariman Bakura da kuma gwamnan na yanzu Yari.
A tsarin, an ruwaito cewa Wakkala a matsayinsa na hannun daman Sanata Yarima, shi ne zai maye gurbin Gwamna Yari, sannan kuma shi Gwamna Yari yam aye gurbin Sanata Yarima a Majalisar Dattawa.
Amma yanzu kwatsam, sai Daily Nigerian ta ruwaito cewa an samu sauyi a tsarin. Sannan kuma Minsitan Tsaro, Mansur Dan Ali ma ya nuna sha’awarsa ta tsayawa takarar gwamnan na Jihar Zamfara.