✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

‘Abin da ya sa muka damu da mutuwar mata yayin haihuwa’

Gidauniyar Sultan da ke yaki da matsalar mutuwar mata yayin haihuwa da sauran matsalolin iyali a jihohin Arewa, ta bukaci karin azama wajen fadakar da…

Gidauniyar Sultan da ke yaki da matsalar mutuwar mata yayin haihuwa da sauran matsalolin iyali a jihohin Arewa, ta bukaci karin azama wajen fadakar da iyali kan muhimmancin yin awo ga mata masu juna biyu da kuma tabbatar da cewa suna zuwa asibiti a lokacin da alamun nakuda suka bayyana.

Gidauniyar wadda aka kafa a shekarar 2014 ta kunshi sarakunan gargajiya da shugabannin addini a matsayin mambobin kwamitin amintattatu na kungiyar a karkashin shugabancin Mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar.

Ko’odinetan Gidauniyar kuma Sarkin Argungu Alhaji Sama’ila Muhammad Mera wanda ya jagoranci sarakuna 19 suka wakilci masarautun jihohin Arewa a yayin wani taro a Abuja a ranar Talatar makon jiya, ya ce gidauniyar ta damu matuka da alkaluman da ake fitarwa daga kafofin watsa labarai kan mace-macen mata wajen haihuwa a yankin da ke cewa a kullum ana rasa kamar mata 200. Ya ce gidauniyar na kokarin tattara bayanai a kan ikirarin ta hanyan amfani da shugabannin unguwanni a duk lokacin da aka samu rahotun mutuwar uwa ko kuma jariri da bai kai wata biyar ba.

Ya ce aikace-aikacen gidauniyar wanda ya hada da rangadi da shirya kwasa-kwasai ga masu fadakarwa da ke da ofisoshin rassa a yankin, ya samu tallafin Naira milaiyan 30 daga Hukumar Kula da Yawan Jama’a ta Majalisar Dinkin Duniya, (UNFPA). Sarakunan sun kuma tattauna kan yadda za su fadada ayyukan gidauniyar a badi.

Taron ya tattauna kan yawaitar matsalar fyade ga yara mata kananan da ake danganta shi da tsubbace-tsubbuce ko sanadiyar tu’ammali da kwaya, inda suka bukaci karin fadakarwa musamman ta bangaren malaman addini. Sauran batutuwan da aka tattauna a kai sun hada da tabbatar da cewa ana gwajin jini a tsakanin masu niyyar yin aure, tare da nuna muhimmancin ba da tazarar haihuwa don samun cikakkiyar lafiya ga uwa da danta gabanin a yaye shi.

Babbar wakiliyar Hukumar UNFP a Najeriya Hajiya Rabi’atu Sageer tana cikin wadanda suka gabatar da jawabi a yayin taron.