Fitaccen jarumin fina-finan Hausa na Kannywood kuma mawaki, Adam A. Zango, ya yi hatsarin mota.
Zango yana tafiya ne a kan hanyarsa ta dawowa daga Jamhuriyar Nijar tare da wasu abokansa, kamar yadda ya wallafa a shafinsa na Instagram.
Sai dai jarumin ya ce “Allah Ya kare su, domin hadarin ya tsaya ne kawai a kan motar da suke tafiya a ciki”. kamar yadda BBC ya ruwaito.
Zango yana yawan yin tafiye-tafiye musamman a lokutan bukukuwan sallah, inda ake gayyatarsa domin yin casu.
BBC ta yi kokarin tuntubar A Zango domin neman karin bayani kan lamarin amma bai amsa wayar ba kawo yanzu.
Amma bayanai a shafinsa na Instagram sun nuna cewa ya je Niyami, babban birnin Nijar, domin yin wasan sallah.