✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

AFCON 2019: Gobe Najeriya za ta kece raini da Libya

A ci gaba da fafatawa a gasar neman hayewa gasar cin Kofin Afirka da zai gudana a Kamaru a badi, gobe Asabar ne ’yan wasan…

A ci gaba da fafatawa a gasar neman hayewa gasar cin Kofin Afirka da zai gudana a Kamaru a badi, gobe Asabar ne ’yan wasan Super Eagles na Najeriya za su fafata da takwarorinsu na Libya a filin wasa na Godswill Akpabio da ke Uyo na Jihar Akwa Ibom.

Wannan shi ne wasa na uku, tun bayan da aka fara gasar.

A wasan da Najeriya ta yi na farko Afirka ta Kudu ce ta bi Najeriya har gida kuma ta lallasa ta da ci 2-0.  A wasa na biyu ne Najeriya ta bi Seychelles har gida ta lallasa ta da ci 3-0 sai kuma gobe da Najeriya za ta hadu da Libya a wasa na uku.

Wasan na gobe zai gudana ne da misalin karfe 4 da rabi na yamma agogon Najeriya a filin wasa na Uyo.

Kawo yanzu Libya ce take saman teburi a Rukunin E da maki 4 sai Afirka ta Kudu ta biyu da maki 4 sai Najeriya a matsayi ta uku da maki 3, sai Seychelles ta hudu wadda ba ta da maki ko daya.

Idan Najeriya ta doke Libiya za ta hada maki 6 ke nan yayin da idan Libya ce ta samu nasara a kan Najeriya za ta hada maki 7.

Masana harkar kwallon kafa suna ganin wasan zai yi zafi ganin duk kasar da ta sake aka doke ta a wannan wasa, to za ta iya fuskantar matsala.

Rabon da Najeriya ta halarci gasar cin Kofin Afirka tun a shekarar 2013, kuma shekarar ce ta lashe kofin a karkashin horarwar marigayi Stephen Keshi.  Ana gudanar da gasar ce duk bayan shekara 2.

Tun farko Hukumar Kwallon Kafa ta Najeriya (NFF) ta bayyana cewa za a yi wannan wasa ne a filin wasa na Ahmadu Bello da ke Kaduna amma daga baya ta canja shawara inda ta mayar da wasan zuwa filin wasa na garin Uyo a Jihar Akwa Ibom saboda wasu dalilai da suka hada da rashin kyan filin wasa na Ahmadu Bello da ke Kaduna.

Sannan a ranar Talata mai zuwa 16 ne Najeriya za ta bi Libya gida don su yi wasa zagaye na biyu.

Don haka wadannan wasanni biyu da za a yi gobe da kuma ranar Talata mai zuwa za su yi tasiri a kasashen biyu.

Duk kasar da ta zama zakara a kowane rukuni ne za ta haye gasar cin Kofin Afirka da zai gudana a Kamaru a shekara mai zuwa idan Allah Ya kai mu.