✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Alamta alamun al’adun al’ummu (1)

Fikar fensirin fanfara Watsattsake na da hakora Tuni ai na lura Wani wuri ai sabuwar sadara Ko a goge shirme a gyaggyara   A zo…

Fikar fensirin fanfara

Watsattsake na da hakora

Tuni ai na lura

Wani wuri ai sabuwar sadara

Ko a goge shirme a gyaggyara

 

A zo a tsattsara

Kare-kare a kakkara

Inda ake bukatar bayani a faskara

Sai  a tattara

Mai karatu yai ta fassara

 

Farin fafutika

Fanninj ilimi a duka

Juhala ake yaka

Kusan kowace dakika

Rani damina da kaka

 

Haruffa

Kalmomi sukan Haifa

Kalm da kalma ke jimla

Adon kawarsu wasulla

Masana sui shakwara da jamfa

 

Babbar riga

Tai fuka-fukin fisga

Falle-falle ta zaga

Zanen asake an tsirga

Kafar wuya da hannaye an tsaga

 

A daura damara

Kokari dai a kara

A zo ai takara

Da safe ake kama fara

Rubutu a zizara

 

Ina mai lage

Da yake ta waige-waige

Baki an wage

Ana kallon tseren bera da mage

Cincin karfi kowa ya dage

 

Ga warkokin watsattsake

Tafiyar tsutsar takun keke

Dashe-dashen shuke-shuke

Kwarakar fadamar rake

Tankar danga a tamke

 

Ai ta hange-hange

Katanga ta kange

Siyasa an kada kuge

Neman mukamai ake ruge-ruge

Tuni wasu sun jibge

 

Bayan  ganuwar gine-gine

Akwai gungun ’yan sane

Da masu mirgine-mirgine

Sui ta tsokane-tsokane

Manufarsu dai an gane

 

Babbaku

Ai fensira sun feku

Rubutu ba nuku-nuku

Rashin fahimta ce turnuku

Sai kawai ai ta zuku

 

Farfaru

Karatu kuru-kuru

Mara bita a sa shi turu

Na-mujiya yai zuru-zuru

Haka ake hana wuru-wuru

 

Hutun hunturu

Hazo-hazo

Ana lalube dabgen kanzo

Kolo mai kwazo

Fatarsa tai fururu

 

Gardin gamba da gafaka

Garnakakin gayunar garka

Garwashin gashin ginsamin girka

Gaggausan gundumin garkame gauraka

Gugar gudumar gwankin gumaka

 

Alaramman almajiran Arewatawa

Mai gamba da gafakar girmamawa

Kiskalin kwamin tilawa

Kaiwa da komowa

Takara ba kakkautawa

 

Kolo da titibiri ake turawa

Aikace-aikacen aikatawa

Abin dundume kururu ake baratowa

Allunansu su zam biyawa

Su zo su zam haddacewa

 

A ingnta yanayin karatu

Tawada ta samu a kurtu

Fekakkiyar gambar rubutu

Zuge da karo su wadatu

Ni kuwa sai in ta satu

 

Masu zabe-zabe

Ku daina labe-labe

Muhimman bukatu za a kebe

Kar a bar almajirai sun rincabe

Tsangaya ai mata yabe

Da siminti ake kwabe

 

Dakuna ai musu dabe

Tsillin matsaloli a kwakkwabe

Damuwar dalibai a kakkabe

Tufafi a sa subulu a sassabe

Da hunturu a basu barguna su lullube

 

 

Tsantsamar fura ta damu

Kayan girki sun samu

A matso ruwan lemu

Mai kwankwada ya jika gemu

Tabahuwa ta shiga jerin kamammu

 

Alamta alamun al’adun al’ummu

Kullun koko da gasarar kamu

Kamun ludayin shan kunu

Na-kanwa akan tsima ungurnu

Wani da tsimin tsamiyar  tsimammu

 

Mai mabudi

Jam’iyyar masu madi

Magarkamar rudi

Ku dai tara zare kui ta kadi

Ko mun daina jin radadi

 

Mai danboto

A rage hadamar koto

Dukiyarmu kar ku sato

Manufarku tuni aka karanto

Muna da cikakken rahoto

 

Kakar zabuka

Ta zababbaka

Wasu nai muku fuffuka

’Yan jagaliya har da duka

Tashin hankali bai da bukka

 

Dan makaranta zabi ka tika

Hakkokin dalibai a saka

Azuzuwa duk sai a leka

Mu duba hotunan da aka lika

Karatu da rubutu duk a surka

 

Ina mai alamar zakara

Makoshinmu yai kara

Ku sanya kasarmu tai cara

Kazarmu ta iya kyarkyara

Bukatarmu dai gyara

A daina kazanta

Mu sabi tsintsiya ta shara

Ta-kwakwa da ’yar laushi a tattara

Mu dai mui ta tsafta

Sai rayuka su faranta

 

Jam’iyyu

Ban da taron yuyuyu

A bari tandar wainarmu ta toyu

Ka da miyagu su boyu

A rage gantsare-gantsare gayu

 

Jibgin jiba a sasshare

Badakala a warware

Idan wani abu ya kakare

Sai a lalubo bakin zare

Sunce kulli ke sa a karkare

 

Mu daina yi wa juna terere

Ko Harare-harare

Kar a karke da hare-hare

Wasu sui ta sare-sare

Tun daga rana zuwa dare

 

Mu kyautata zaman tare

A kiyayi a-ware

Kar kasa ta dare

Al’umma ta jure

A haskaka fitilu farare

Ba sauran fitinu

Murdin ciki ake sha wa ungurnu

Sakiya ai wa mai kurkunu

Lumana ke sa a zam zaunannu

Kasarmu tai karfin ginin ginannu

 

Kowa sai ya more

Mai-duka dai ya hore

Cutuka duk Ya kare

Al’umma ta murmure

Wurgar  da masu nufin ta-bare