✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Alhaji Umaru Nagwaggo ya zama Baselu na Atowori

An nada Alhaji Umaru Nagwaggo a matsayin Babaselu na kasar Atowori wato kamar sarautar dan Madami a kasar Hausawa. Sa’ilin da  yake nada masa mukamin, …

An nada Alhaji Umaru Nagwaggo a matsayin Babaselu na kasar Atowori wato kamar sarautar dan Madami a kasar Hausawa.
Sa’ilin da  yake nada masa mukamin,  Oba Olarewaju na  Atowori  ya ce akwai dimbin Hausawa da ’yan Arewa mazauna garin, amma irin rawar da Alhaji Umaru Nagwaggo ke takawa, ya ci a ba shi  sarautar  ma da ta fi  ta Babaselu.
Oba  Olarewaju ya yi  fata sarautar ta kara  wa  Alhaji Umaru kwarin gwiwar  ci gaba da ayyukasa na cigaban al’ummar Atowori,  musammam na ganin yadda ake  kara  samun dankon  zumunci   tsakanin Hausawa da Yarbawa   da ma sauran kabilun da ke zaune a tsakanin al’ummar.
Oba ya ce  Alhaji Umaru  ne ya kaddamar da taron lokaci-lokaci tsakanin  masarautar  da  sauran  jama’ar  wannan wurin,  ta  yadda  za a kankare  kabilanci   tsakanin  mutanen  da ke  zaune a wurin, “Kuma tun  daga lokacin muka yi  ban kwana da  duk  wani  abu da ake cewa  tashin hankali  ko kuma  rashin    fahintar  juna”. Inji shi.
Da yake jawabinsa na godiyar  ba shi  wannan mukamin, Alhaji Umaru Nagwaggo ya ce wannan karramawar za ta kara  masa kaimi  wajen  kara  ayyukan cigaban al’ummar, saboda shi ma  ya  zama dan kasa, musamman ma da yake ya kwashe  shekaru 24  yana zaune  cikin  wadannan mutanen.
Ya ce  kuma tun daga  wancan lokacin zuwa ranar da aka ba shi  wannan sarautar  zaune  yake da daukacin jama’ar  cikin lumana,  musammam  ma  yanzu  da harkokin tsaro,  a wasu  sassan Najeriya,  musamman  a Arewa, suka tabarbare. “Tun daga lokacin da na fara  mu’amala da  jama’ar  da ke wannan wurin nake  musu nasiha da su kankare kabilanci a zukatansu   kuma  su  dauki  juna ’yan uwa kuma  hakan  ya yi  tasiri  kwarai   da  gaske”. Inji shi.
Alhaji  Umaru ya ce da a ce ’yan siyasa  da ma  shugabannin  addini  za su  rika jaddada bayanan  da ka kankare  kabilanci  a cikin al’umma,  kana   gwamnati  ta  rika daukar  matakin ba-sani-ba-sabo  ga  duk  wanda  ya  aikata  ba daidai ba, to da  an samu  daidaituwar  al’umma  kuma  batun jaddada kabilanci  da  rikicin  addini  da sun ragu ainun.