An birne gawarwakin mutum 18 da ‘yan bindiga suka yi wa kisan gilla yau Laraba a kauyen `Yar Gamji a karamar hukumar Batsari jihar Katsina.
An birne gawarwakin ne a makabartar Dan Takum bayan yi masu sallar jana’iza a fadar Sarkin Katsina, Abdulmumini Kabir Usman, Hakimai da wasu masu rike da sarautu tare da jami’an gwamnati da kuma sauran jama’ar gari suka halarcin sallar jana’izar.
Limamin babban masallacin Katsina, Ustaz Mustapha Ahmed, ne ya jagorancin sallar jana’izar.