An fitar da Jadawalin Gasar Cin Kofin Nahiyar Afirka na ’yan wasan da ke taka-leda a gida ta bana (CHAN 2020,) inda mai masaukin baki, Kamaru, za ta fafata da Zimbabwe a bikin bude gasar ranar 4 ga Afrilu mai zuwa.
Sashin Hausa na Rediyon BBC ya ce, Indomitable Lions za ta fafata da Zimbabwe ne a filin wasa na Ahmadou Ahidjo, wanda a nan ne za a buga karawar karshe ranar 25 ga watan Afrilu.
Mai rike da kofin kasar Moroko za ta fara karawa ce da Togo ranar 6 ga Afrilu, kafin ta fafata da Rwanda da Uganda a rukuni na uku.
Gasar ta CHAN da za a yi wadda ta kunshi ’yan wasa da ke taka-leda a gida ta sa an sauya lokacin kare gasar Zakarun Afirka ta Champions League da ta Confederation Cup zuwa wata biyu.