Hukumar Shigi da Fici wato magireshan a Jihar Katsina sun kama wasu mutane da ake zargi suna safarar mutane zuwa kasashen waje.
Kwanturolar hukumar na Jihar Katsina, Mista Ajisafe Joshua Olusola ne ya bayyana wa manema labarai hakan a lokacin da yake gabatar da masu laifin.
An kama Monday Adeoye Olampekun mai shekara 49 dan asalin Jihar Ondo da wasu mutane uku.