✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An kara ranakun fita a jihar Ogun

Za a rika walwala a ranaku biyar a yi kullen kwana biyu a jihar.

Gwamnan jihar Ogun Dapo Abiodun, ya sauya salon dokar kulle a jihar.

Dapo Abiodun ya takaita dokar kullen zuwa ranaku Asabar da Lahadi maimakon ranaku hudu da ake kullen a baya.

A jawabinsa kai tsaye ga jama’ar jihar ranar Alhamis, gwamnan ya ce za a ba al’ummar jihar damar fita su yi walwala a ranakun Litinin zuwa juma’a daga karfe 6 na safe zuwa 8 na dare.

Ranakun Asabar da Lahadi kuma za su ci gaba da kasancewa ranakun kulle a jihar.

A baya dai ana bai wa jama’ar jihar damar fita suyi walwala ne a ranakun Litinin, da Laraba da kuma ranar Juma’a.