A wani sabon hari da ‘yan bindiga suka kai unguwannin kananan hukumomin: Dan Musa, Faskari da Batsari a jihar Katsina.
Rahotanni da dama sun bayyanawa majiyarmu cewa, ‘yan bindigar sun kai harin ne akan babura inda suka dinga kashe duk wanda suka samu.
A yankin Sabon Layin Galadima da ke karamar hukumar Faskari sun kashe akalla mutum 11.
Sai dai kakakin hukumar ‘yan sandan jihar SP Gambo Isah ya ce, mutum daya aka harba kuma yana asibiti ana yi masa jinya.