Rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi ta kashe mutum biyu da ake zargin ‘yan fashi da makami ne tare da tarwatsa maboyar masu garkuwa da mutane a Karamar Hukumar Alkaleri da ke Jihar.
Jami’an sun yi hakan ne bayan sa’o’i 48 da kashe wani dan fashi da makami a wani samame da suka kai kauyen Miri cikin karamar Hukumar Bauchi.
Jami’in hulda da jama’a na Hukumar ‘yan sandan jihar DSP Kamal Datti Abubakar, ne ya sanar da hakan a Bauchi, ya kuma ce jami’an ‘yan sandan sun kwato makamai da dama a samamen da suka kai maboyar.