Rahotanni na bayyana cewa, an kai hari masallatai biyu na juma’a lokacin sallar Juma’ar yau inda maharan suka kashe mutum 49 da raunata mutum 20 masallatan da suke birnin New Zealand.
Firayi Ministan New Zealand Jacinda Ardern, ya yi Allah wadai da wannan harin kuma ya kwatanta wannan harin a matsayin harin ta’addanci, ya ce ranar yau ta bakin ciki ce ga ‘yan kasar.