✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An sace dalibai mata 6 da malamai 2 a Kaduna

Wasu ‘yan bindiga sun sace wasu dalibai mata su shida da malamai biyu a makarantarsu da ke garin Kakau Daji, karamar Hukumar Chikun a jihar…

Wasu ‘yan bindiga sun sace wasu dalibai mata su shida da malamai biyu a makarantarsu da ke garin Kakau Daji, karamar Hukumar Chikun a jihar Kaduna.

Rahotan na cewa, an yi awon gaba daliban da malaman makarantar mai zaman kanta a lokacin da ‘yan bindigar suka shiga makarantar a cikin daren Laraba da misalin karfe 3:00 na tsakar dare.

Rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna ta tabbatar da aukuwar kai harin makarantar mai suna ‘Engravers College’ inda jami’an ‘yan sandan suka ce, sun samu rahoton da safiyar yau Alhamis game da harin ‘yan bindigar da suka cikin makarantar, inda suka tafi da daliban da malamansu biyu.

Kamar yadda jami’in hulda da jama’a na Rundunar ‘yan sandan jihar DSP Yakubu Sabo, ya tabbatar.