Rahotanni daga jihar Taraba na bayyana cewa, gwamnatin jihar Taraba ta saka dokar hana fita sakamakon rikicin da yake son barkewa, an sa dokar ne ta tsawon sa’o’i 24 a yau Talata.
Babban maiba gwamnan jihar Darius Ishaku shawara akan watsa labarai Mista Bala Dan Abu ne ya sanar da hakan, don samun zaman lafiya a birnin.