An sako Alkalin babbar kotun jihar Ondo Mai shari’a Abdul Dogo, wanda aka yi garkuwa da shi kwana biyar da suka wuce.
An dai sako Abdul ne da misalin karfe 2 na tsakar daren ranar Asabar.
Rahoton bai bayyana an biya kudin fansa ko kuma ba a biya ba.
Masu garkuwa da mutane sun sace alkalin ne a garin Ibilo da ke iyakar jihar Ondo da jihar Edo a ranar Talata.