✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An samu jinkirin dawo da ‘Yan Najeriya gida daga Afirka ta Kudu

An samu jinkirin dawo da ‘yan Najeriya gida daga kasar Afirka ta Kudu a jirgin kamfanin Air Peace Airlines sakamakon jinkiri wajen binciken tantance wadanda…

An samu jinkirin dawo da ‘yan Najeriya gida daga kasar Afirka ta Kudu a jirgin kamfanin Air Peace Airlines sakamakon jinkiri wajen binciken tantance wadanda za a dawo da su.

A cewar jami’an ma’aikatar kasashen waje da ke birnin Johannesburg da ke Afirka ta Kudu, na cewa an tsara tashin jirgin Air Peace da ‘yan Najeriyar da misalin karfe 9 na safiyar yau, amma har yanzu jirgin bai tashi da kowa ba yana kasa.

Jami’an sun ce, an tantance fasinjoji 84 cikin 313 cikin rukunin farko da za a dawo da su gida Najeriya a yanzu haka.

Sai dai jami’an tsaron shige da fice na kasar sun ce an samu jinkirin ne, sabod matsalar na’urar tantancewar.