An samu rahoton mutuwar mutum biyu bayan wani ruwan sama mai karfi da aka yi da ya kai awa daya, wanda ya yi sanadiyyar ambaliyar a manyan hanyoyin Uyo babban birnin jihar Akwa Ibom.
An gano gawar namiji da mace a cikin kwata a layi mai suna Atiku Abubakar lane kusa da gidan man fetur na GWT a Uyo. An fara ruwan da misalin karfe 5:30 na yamma zuwa 6:45 na yamma a jiya Lahadi.
Wata ganau mai suna Misis Uduak Mbakara ta ce, an gano gawar wadanda suka rasun ne a safiyar yau Litinin. Daga nan makwabtan wurin suka sanarwa ‘yan sanda gawar mutanen da suka gani.