✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An yi garkuwa da malamin kwalejin Hassan Usman Katsina

An yi garkuwa da malamin tsangayar koyar da ilimin sana’a da ke Kwalejin kimiyya da fasaha ta Hassan Usman mai suna Dakta Bello Birchi. Masu…

An yi garkuwa da malamin tsangayar koyar da ilimin sana’a da ke Kwalejin kimiyya da fasaha ta Hassan Usman mai suna Dakta Bello Birchi.

Masu garkuwan sun gaba Dakta Bello ne a gidansa da tsakar daren jiya Laraba a kauyen Tashar Bara’u hanyar Dutsinma ta jihar Katsina.

Shugaban kungiyar malaman Kwalejin kimiyya da fasaha ASUP Dakta Sabi’u Yau Abdullahi, ya tabbatar yin garkuwa da malamin.