An yi garkuwa da malamin tsangayar koyar da ilimin sana’a da ke Kwalejin kimiyya da fasaha ta Hassan Usman mai suna Dakta Bello Birchi.
Masu garkuwan sun gaba Dakta Bello ne a gidansa da tsakar daren jiya Laraba a kauyen Tashar Bara’u hanyar Dutsinma ta jihar Katsina.
Shugaban kungiyar malaman Kwalejin kimiyya da fasaha ASUP Dakta Sabi’u Yau Abdullahi, ya tabbatar yin garkuwa da malamin.