An yi jana’izar Manajan Kungiyar Kwallon Kafa ta Kano Pillars Malam Kabiru Baleriya a shekaranjiya Laraba, bayan ya rasu a yammacin ranar Talata a wani asibiti mai suna Doctor’s Clinic da ke Bompai, a birnin Kano.
A ranar Talata ce wata sanarwa da kulob din ya fitar ta ce, Baleriya ya rasu yana da shekara 57, kuma ya rasu ya bar matarsa da ’ya’ya shida.
“Marigayi Baleria ya taba buga wa kungiyar kwallon kafa ta kasa kwallo. Sannan ya taba horar da kungiyoyin kwallon kafa na kasa da ’yan shekara 17 da kuma ’yan kasa da shekara 20. Baleriya ya rasu ne bayan ya yi fama da jinya,” inji sanarwar
Masoya kwallon kafa da dama sun yi ta tururuwa zuwa gidansu da ke Durumin Zungura, a birnin Kano don yi wa iyalansa da ’yan uwansa ta’aziyyar rashinsa.
Baleriya dai ya taba zama Kocin Kano Pillar na wucin gadi kafi daga bisani ya zama Manajan kungiyar.