Jam’iyya mai mulkin Najeriya APC ta bukaci kotun koli da ta kori Gwamnan jihar Sakkwato Aminu Waziri Tambuwal daga mukaminsa sakamakon binciken tuhumarsa da ake yi akan aikata wasu laifuka a zaben fidda gwani na shekarar 2014 wanda hakan yasa jam’iyyar ta tsai da shi a matsayin dan takarar Gwamnan jihar na jam’iyyar.
A yanzu dai APC tana goyon bayan abokanan takatar neman kujerar Gwamnan jihar, Sanata Umar Dahiru da Aliyu Abubakar Sanyinna da suka daukaka kara akan zaben da aka yi wa Gwamna Tambuwal bayan zaben.