Hukumar zabe ta jihar Kebbi (KESIEC), ta sanar da sakamakon zaben Kananan Hukumomin jihar da aka yi ranar a 26 ga watan Oktoba 2019 yayin da jam’iyyar APC tayi nasarar lashe zaben a dukkanin Kananan Hukumomin jihar, kamar yadda shugaban hukumar zaben Jihar Alhaji Aliyu Mera, ya sanarwa manema labarai yau Alhamis.
“Jam’iyyar APC ita ce tayi nasarar lashe zabukan da aka gudanar a dukkanin kanan hukumomi 21 na jihar. Jam’iyyun PDP da FP da sauran abokan karawa basu yi wani abin azo a gani ba a zaben.” in ji shi.
Ya kara da cewa, an gudanar da zaben cikin kwanciyar hankali ba tare da hatsaniya ba, kuma an bayyana sakamakon a gaban wakilan kowace jam’iyya.