✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Atiku ya yi alakawarin inganta noma da kasuwanci idan aka zabe shi

Tsohon mataimakin shugaban kasar Najeriya kuma dan takarar shugaban kasar Najeriya a jam’iyyar PDP Atiku Abubakar, ya yi alkawarin inganta noma da harkokin kasuwanci idan…

Tsohon mataimakin shugaban kasar Najeriya kuma dan takarar shugaban kasar Najeriya a jam’iyyar PDP Atiku Abubakar, ya yi alkawarin inganta noma da harkokin kasuwanci idan aka zabe a matsayin shugaban kasar Najejriya.

Dan takarar ya bayyana hakan ne yayin kaddamar da yakin neman zabensa a filin wasa na Sani Abacha jihar Kano. Atiku  ya bayyana irin rashin jin dadinsa game da durkushewar masana’antu a  duk fadin Najeriya kuma ya dauki alwashin farfado da su idan har ya lashe zaben shugaban kasar Najeriya.