✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Bambamin bilinbituwar birkitattun batutuwan barkwanci

Bambamin baka Burgar burge mutumin bukka Shaci-fadin sa shakku Walwalar mai tsigi da tukku Bututun batun raraka   Daga Lantsadan aka zo da akwaku Baban-bakin…

Bambamin baka

Burgar burge mutumin bukka

Shaci-fadin sa shakku

Walwalar mai tsigi da tukku

Bututun batun raraka

 

Daga Lantsadan aka zo da akwaku

Baban-bakin ce-ce-ku-cen Birtaniyawa

Ya hada takarar kokowa

Har da uwargida mai dawa

Tumbin-Giwa akai kamun kazar kuku

 

Yaren yarfin yarfe

Yawar yagalgala yafe

Yaki da yunwa ake wa dafe-dafe

Yankwanewar laulayi a daddafe

Yamutsin yakicewa a kife

 

Taro ya cika ya batse

An yi tande-tande an gyatse

’Yan takara sun kotse

Masu akwaku sun hantse

Da kammalawa kowa ya waste

 

Birkitattun batutuwa

Birgimar bagararwa

Bini-binin bilinbituwa

Basajen bututun busawa

Banga-bangar bubbugawa

 

Babban bakin ce-ce-ku-ce

Yai takaddama makon da ya arce

Maza karamin lauje da mace

Hana masu ciki mace-mace

Farfado da farfajiyar ilimin da ke mace

 

’Yan takara

Da masu taka-kara

Su kai ta kara

Wajen bijiro da batutuwa karara

An dai karkare ba harara

 

Gunsar gintsewar gyatsa

Mai fuka-fukin tashi yai kwankwatsa

Kallabin rawuna tai gatsine gatsa-gatsa

Da Uban masu kwankwatsa

Ya yunkura kamun kifi da fatsa

 

Birnin Dabo

Kun san ba a dabo

Balle zari ruga da kwabo

Tsoho da sabo

Gwamnati ba ta sabo

 

Kun dai tallata manufofi

Ku bar yi wa juna yarfi

Kar ku maishe da talakawa makafi

Nagarta an fasko wanda ya fi

Masu ji da na-zomo sun yi tafi

 

Mu dai mun taru a shigifa

farfajiyar jami’a mai rumfa

Babban-bakin-ce-ce-ku-ce yai musaffa

Daga Lantsandan aka bude kafa

Haurobiyawa a dai yi kaffa-kaffa

 

Gwamnan gundumar gandun aiki

Gararumar gyaran girki

Ginsamin gwabjejen miki

Gangamin ban mamaki

Gwanintar gujewar mai mulki

 

An tuna da almajirai

Da talakawa fakirai

Inganta rayuwar jarirai

Murmurewar uwar-jiki ceton rai

A dai gyara kura-kurai

 

Za a hana dirshan din kashe fatarai

Kwayoyi sun jefa gayu hadari

’Yan lalle da Adon-gari

Kui aiki nagari

Kar ku afka garari

 

A daina kaso-kason wawanci

Damfarar damalmala kasuwanci

Cinikin ci-mu-ci

Carafken ci da gumjn mai kawaici

An dan jinka masa tukuici

 

Damo-da-kura-da-diyya

Dama-damar-kurda-kurdar-tsiya

Jam’iyyun jar-miyya

Jimamin jin jikin juriyyar jiniya

Daura damarar daukar dawainiya

 

Masu fuka-fukin tashi

Kar ai muku wa-ka-ci-ka-tashi

Kuna ta tsimayin kwasar adashi

Zakuwa ta sa ku hanzarin tashi

Mulki na biya ba bashi

 

Budurwa ai mata toshi

Daushen goro sa bakin tsohuwa washi

Maigida kar ka hada kashi

Cefane ke sa uwargida karsashi

Ta gama tai kwalliya da kunshi

 

Saisaita salon siyasa

Sunce sasarin sa-in-sa

Sasanta sabanin rashin sani

Sahalewar al’umma aiki da sani

Sarewar sanyaya saiwoyin sassa

 

Asibicin makon da ya arce, wato ranar karamin lauje ga watan Fafe-baure na shekara ta dubu karamin lauje da sili da manuniyar kasa, Babban-bakin-ce-ce-ku-cen Birtaniya ya shirya karon-battar kalallame kalaman ’yan takarar Gwamnan Jihar Tumbin-giwa a shigifar farfajiyar Jami’ar Mai martaba na birnin Dabo, cikin wata katafariyar rumfa da zimmar ganin ba a yi wa mutane rufa-rufa ba.

’Yan takara da masu taika-karar da aka gayyato sun hada da Mai fuka-fukin tashi da ya yi GUMTSAR GINTSEWAR GYATSA, sai Malam TATTAKIN-TAKUN-KAI, da MUMINAR MANAGARCIYAR MACE MAI MANUFA, wato Uwargida Gwamna Gwamma Gwaggon al’umma. Daukacin wadannan ’yan takara da jam’iyyunsu na hankoron darewa bisa karagar mulkin Jihar Tumbin-giwa a birnin Dabo, inda ba a dabo.

Daukacin mumbarin kowane/kowace dan/’yar takara an alamta alamun al’adun al’umma, ko in ce tambarin jam’iyya.

Wani abin ban ta’ajibi shi ne daukacin mutanen da suka tafka takaddama a shigifar jami’a, sun bibiyi kadin tsilli-tsillin matsalolin al’umma, wadanda suka hada da yadda za a inganta farfajiyar Bokan Turai da harkokin koyon watsattsake da fallen shafukan wagagen littattafai. Kusan kowane daga jerin wadanda suka fafata a takaddamar ce-ce-ku-cen da zarar ya/ta fara kwakwazo kai ka ce da an mika musu ragamar mulki, shi ke nan al’umma za ta ci AWARA TA WARWARE. Ga dukkan alamu dai sai an gwada akan san na-kwarai. Masu wasan Samson-siya-siya da kwakwalwar talakawa a daina zuki-ta-malle kama-kare ka hada shi da zomo.

Babban abin takaici dai a wannan takaddamar ce-ce-ku-ce da aka tafka, shi ne kin halartar Gwamnan Gundumar Gandun aiki; sai kuma daukacin ’yan takarar da ke hankoron darewar karagar mulki, kusan duk a cikin birni za su aiwatar da tsare-tsaren ayyukansu. Saboda haka sai mu ce al’ummar karkara ko oho!

Sannan babu wani daga jerin jam’iyyun jar-miyya da ya kudiri koyi da kyawawan manufofin Baban-burin-huriyya, musamman yadda gwamnati mai ci ke ta fafutikar dundume kururun ’yan dugwi-dugwi da ke kwankwadar fura-mai-kyau a farfajiyar koyon watsattsake da buda wagagen littattafai matakin farin-farawa. Shirin kawar da dirshan din kashe fatari a tsakanin masu fuka-fukin tashi, musamman wadanda aka yaudare su suke ta zuba adashin, ranar kwasa sai a jinka musu jagwalgwalon sa-in-sar siyasar jagaliya

Batu na ingarman karfen karafan titin tarragon layin dogo, ba tare da bata lokacin wulwulawar hannayen agogo ba, duk wani dan takara da ya yi tuya ya manta da albasa mai lawashi, tabbas sai mu ce daukacin batutuwansa/ta an karke ne kawai da BIRKITATTUN BATUTUWAN BILINBITUWAR BARKWANCI. Kuma nagartar kowane dan takara tuni Haurobiyawa sun fasko, don haka babu wanda zai cusa musu duhun kurungu a sako.