A wani rahoto da kafar Goal.com ta ruwaito daga Le10Sport, an ruwaito cewa Real Madrid da Barcelona na zawarcin dan wasan gaban Najeriya, Victor Osimhen wanda yanzu haka yake taka leda a kungiyar Lille ta Faransa.
Osimhen dai bana tauraronsa na matukar haskawa, musamman a Gasar Ligue 1 ta Faransa.
Sannan kuma tun zuwansa kungiyar ta Lille daga Sporting Charleroi na kasar Belgium ya zura kwallaye 16 a duk wasannin da ya buga, ciki har da 11 da ya zura a wasannain 21 da ya buga a Gasar Ligue 1.