A yau Alhamis shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, yana ganawar sirri da manyan hafsoshin tsaron Najeriya a fadarsa Abuja. Ganawar dai na zuwa ne bayan gwamnatin tarayya ta umarci Shugabar Mai’aikatan Gwamnatin Tarayya Misis Winifred Oyo-Ita da ta aje aikinta.
Shugabar, ta aje aikin ne don a samu damar binciken zamba da ake zargin ta da shi.
Ya zuwa yanzu ba a bayyana dalilin ganawar da shugaban yake yi da hafsoshin tsaron ba. Kamar yadda Kamfanin Dillancin Labarai NAN ya sanar.