✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Buhari ya mika wa majalisa sunan sabbin alkalai 11

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen sabbin alkalai 11 da zai nada a Babbar Kotun Birnin Tarayya da ke zamanta a…

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen sabbin alkalai 11 da zai nada a Babbar Kotun Birnin Tarayya da ke zamanta a Abuja.

Buhari ya sanar da majalisar ne ta cikin sakonsa da Shugaban Majalisar Ahmed Lawan ya karanta wa takwarorinsa a zamansu na ranar Talata.

“Kamar yadda Sashe na 256(2) na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na 1999 ya yi tanadi, ina neman amincewar Majalisa da sunayen nan guda 11 a matsayin Alkalai a Babbar Kotun Birnin Tarayya, Abuja”, inji wasikar.

Sabbin wandanda za a nada din da jihohin da suka fito su ne:

  • Abubakar Husseini Musa (Adamawa).
  • Edward Okpe (Binuwai).
  • Babashani Abubakar (Borno).
  • Emuesiri Francis (Delta).
  • Jude Ogho (Delta).
  • Josephine Enobi (Edo).
  • Christopher Opeyemi Oba (Ekiti).
  • Mohammed Idris (Kano).
  • Hassan Maryam Aliyu (Kebbi).
  • Fashola Akeem Adebowale (Legas).
  • Da kuma Hamza Muazu (Neja).