Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen sabbin alkalai 11 da zai nada a Babbar Kotun Birnin Tarayya da ke zamanta a Abuja.
Buhari ya sanar da majalisar ne ta cikin sakonsa da Shugaban Majalisar Ahmed Lawan ya karanta wa takwarorinsa a zamansu na ranar Talata.
- Majalisa na bincikar NNPC kan Dala biliyan 1.05
- Wadume: Kotu ta dage sauraron shari’ar ta’addanci
- Fassara ta sa dage shari’ar Shehu Sani a kan sayen alkalai
“Kamar yadda Sashe na 256(2) na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na 1999 ya yi tanadi, ina neman amincewar Majalisa da sunayen nan guda 11 a matsayin Alkalai a Babbar Kotun Birnin Tarayya, Abuja”, inji wasikar.
Sabbin wandanda za a nada din da jihohin da suka fito su ne:
- Abubakar Husseini Musa (Adamawa).
- Edward Okpe (Binuwai).
- Babashani Abubakar (Borno).
- Emuesiri Francis (Delta).
- Jude Ogho (Delta).
- Josephine Enobi (Edo).
- Christopher Opeyemi Oba (Ekiti).
- Mohammed Idris (Kano).
- Hassan Maryam Aliyu (Kebbi).
- Fashola Akeem Adebowale (Legas).
- Da kuma Hamza Muazu (Neja).