Shugaban Najeriya Buhari ya sanar da sauya sunan filin wasa na kasa da ke Abuja zuwa MKO Abiola, mutumin da aka yi imanin cewa shi ne ya lashe zabe na 1993 wanda gwamnatin sojin wancan lokacin ta soke.
Shugaban ya sanar da hakan ne yau a jawabinsa na ranar Dimokradiyya.
An sauya ranar dimokradiyya daga 29 ga watan Mayu domin tunawa da kuma rage radadin alhinin soke zaben shugaban kasa na 1993.