Shugaba Muhammadu Buhari, zai rantsar da sabbin Ministocinsa 43 ranar 21 ga Agustan da muke ciki bayan tantace su da majalisar dattawa ta yi.
Jami’in ofishin Sakataren gwamnatin tarayya Mista Babatunde Lawal, ne ya sanar da hakan a yau Talata.
14 daga cikin 43 na Ministocin sun yi aiki da Shugaba Buhari a wa’adinsa na farko a matsayin Ministoci.