✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Burin neman matsayi bai kai dan takara ga nasara a Najeriya- Kashim Shetima

Tsohon Gwamnan jihar Borno kuma Sanata a yanzu mai wakiltar Borno ta Arewa, Kashim Shetima ya gargadi ‘yan siyasa da su yi taka-tsantsan wajen neman…

Tsohon Gwamnan jihar Borno kuma Sanata a yanzu mai wakiltar Borno ta Arewa, Kashim Shetima ya gargadi ‘yan siyasa da su yi taka-tsantsan wajen neman mukamin siyasa ta ko a mutu ko a yi rai.

Sanata Shetima, ya bayyana bukatar ce, a yayin taron tattaunawa ta shekara-shekara da kamfanin jaridun Media Trust masu jaridar Aminiya, ya shirya a yau Alhamis a Abuja, wato ‘Trust Annual Dialogue’, inda taken taron wanda shi ne karo na 17 ya maida hankali a kan shekara 20 da dawowar dimokoradiyya a Najeriya.

Ya ce, idan a ka duba tarihin tsayawa takarar shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya nemi matsayin shugabanci sau 3 ba tare da nasara ba, sai a na 4 ne ya samu nasara bayan an tilasta masa sake tsayawa takara.

“Haka nan wanda ya gabace shi shugaba Goodluck Jonathan burinsa shi ne ya tsaya takarar shugaban karamar hukuma, sai gashi a karshe ya samu, tare da nasara a na mataimakin gwamna, ya kuma yi gwamna, ya yi mataimakin shugaban kasa, sannan ya yi shugaban kasar ba ki daya.

A lokacin da ya nuna burin sai ya zarce, sai ya sha kasa. Shi kansa marigayi shugaban qasa Umaru ‘Yar Aduwa, burinsa shi ne ya koma koyarwa a jami’a bayan gwamna a jihar Katsina, amma sai gashi ya zama shi ne shugaban kasa a zaben da ya biyo bayan hakan.

Haka nan ya ce, ya kamata ‘yan takara su san da cewa, “A cikin adadin wadanda za su tsaya takara, mutum daya ne kadi a karshe zai yi nasara.