✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Cancanta za mu duba wajen daukar ma’aikata – Kyari

Sabon Shugaban Kamfanin Man fetur na Kasa (NNPC), Malam Mele Kolo Kyari, ya ce kwarewa da cancanta ne abin da  kamfanin zai duba wajen daukar…

Sabon Shugaban Kamfanin Man fetur na Kasa (NNPC), Malam Mele Kolo Kyari, ya ce kwarewa da cancanta ne abin da  kamfanin zai duba wajen daukar ma’aikata ba sanayya ba.

A kwanan nan kamfanin man na ya gudanar da jarrabawar daukar ma’aikata daga duk fadin kasar nan wacce dubban mutane suka rubuta.

Malam Kolo Kyari ya kara da cewa, a karkashin jagorancinsa, za a fara aikin lalubowa da tatsar albarkatun mai da suke a jihohin Arewacin kasar nan ba da jimawa ba.

“Shugaban Kasa ya ba mu ikon cewa duk inda mai yake a kasar nan mu nemo shi kuma mu fara dibarsa don sarrafawa da wadatar da al’umma da man mai rahusa ga talakawa,” inji Kyari

A cewarsa, tun a ’yan watannin baya Shugaba Muhammadu Buhari, ya ziyarci wani gari da ake kira Kwalmani da ke tsakanin jihohin Bauchi da Gombe, don ganin irin arzikin mai da ake da shi a yankin.

“Nan ba jimawa ba za mu sanar wa duniya adadin yawan man da albarkantun man da ake da su a yankin,” inji shi.

A cewar Kyari, duk wanda ya taka doka, za a ladabtar da shi yadda doka ta tanada, yana mai cewa babu wanda zai dauki doka a hannunsa a karkashin shugabancinsa.