✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Chelsea ta fara zawarcin Isco

Rahotanni da ke fitowa daga kulob din Real Madrid na Sifen sun ce dan kwallon gaba a kulob din Isco yana yunkurin barin kulob din…

Rahotanni da ke fitowa daga kulob din Real Madrid na Sifen sun ce dan kwallon gaba a kulob din Isco yana yunkurin barin kulob din a watan gobe idan aka bude kasuwar cinikin ’yan kwallo.

Kulob da dama ne suke zawarcinsa, ciki har da Chelsea da na Manchester City a Ingila.  Amma alamu sun nuna Chelsea ce ta fi zakewa don ganin ta dauke dan kwallon.

Rahotanni sun ce Chelsea ta taya dan kwallon a kan Fam miliyan 70 (kimanin Naira biliyan 33) kuma tana sa ran biyansa albashin Fam dubu 250 (kimanin Naira miliyan 117) a kowane mako.

Jaridar  The Sun ta Ingila ta ce, Isco wanda wasanni 11 kacal ya buga wa kungiyar Real Madrid a gasar La-Liga ta bana, ya zaku ya bar kulob din a watan Janairu ganin yadda yake yawan zama a benci.

A ranar da kulob din CSKA Mosko ya doke Madrid da ci 3-0 a gasar Zakarun Turai magoya bayan Madrid sun rika yi masa ihu, al’amarin da ya sa ya yanke shawarar barin kulob din.