✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Sakamakwon Zaben Gwamnonin Najeriya Na 2023 (Alkaluma Daga:INEC)

Coronavirus ba ta kama ni ba —Ahmed Musa

Dan wasan tawagar kwallon kafa ta Super Eagles ta Najeriya, Ahmed Musa, ya musanta labarin da ke wadari a kafafen sadarwa na zamani cewa ya…

Dan wasan tawagar kwallon kafa ta Super Eagles ta Najeriya, Ahmed Musa, ya musanta labarin da ke wadari a kafafen sadarwa na zamani cewa ya kamu da cutar coronavirus.

Ahmed Musa ya karyata labarin ne, wanda ya kira labaran bogi, a shafinsa na Twitter.

“Ku yi watsi da duk wani labarin karya da cewa ni ko iyalina mun kamu da cutar COVID-19.

“Mun dai killace kanmu na tsawon mako biyu kasancewar ba mu jima da shigowa ba daga Saudi Arebiya”, inji Ahmed Musa, wanda ke wasa a kungiyar kwallon kafa ta Al-Nasr da ke Saudi Arebiya.

Ya kuma mayar da martini ga wani sakon Twitter (wanda aka cire daga bisani) da ke ambato shi yana cewa ya kamu: “Cire wannan labarin bogin don Allah”.

Dan wasan ya kuma yi kira ga masu bibiyar sa a shafin na Twitter da su bi tsarin nisa da juna su kuma kaurace wa labarin bogi.