Rahotanni na bayyana cewa, akalla mutum 21 ne suka kamu cutar amai da gudawa a jihar Borno da kuma mutum tara a jihar Yobe kamar yadda hukumarlafiya ta duniya ta sanar.
Akwai alamar raguwar masu dauke da cutar a jihar Borno yayin da ake samun karuwar masu dauke da cutar a jihar Yobe.
Yankunan da suke dauke da cutar a Borno sun hada da kananan hukumomin Jere, Maiduguri, Konduga da Guzamala. Yayin da rahotan ya sanar da cutar a garin Gulani da yankunan shida na Damaturu.