Kotun koli ta dage yanke shari’ar jihohin: Kano da Bauchi da Sakkwato da Benuwe. Sai kuma sauran jihohin Imo da Filato.
Dalilin da yasa kotun koli ta dauki matakin dage zaman shari’ar da za a yi yau Litinin. Sun hada da: Daya daga cikin alkalai bakwai da za su yanke hukuncin ba shi da lafiya.
Ma’aikatan kutun sun ce hukunce-hukuncen da kotun za ta yanke sun yi yawa, kuma wasu hukunce-hukuncen za a yanke ne bayan an saurari lauyoyin bangarorin biyu.
Rahotanni daga kotun na cewa magoya bayan wadanda lamarin ya shafa sun cika kotun makil.
Kotun ta bayyana cewa a gobe Talata za a ci gaba da zaman.