Dan Majalisar da ke wakiltar mazabar Toro da Jama’are a Majalisar Dokoki ta Jihar Bauchi, Tukur Ibrahim ya kamu da cutar coronavirus.
Kakakin Majalisar Abubakar Sulaiman ya bayyana hakan yayin zamansu na musamman a ranar Litinin bayan dawowarsu daga hutu.
A cewarsa, yanzu haka Tukur Ibrahim na a daya daga cikin cibiyoyin killace masu cutar a jihar inda yake samun kulawa.
Kakakin majalisar ya ce tuni aka dauki jinin wasu daga cikin ‘yan majalisar domin su ma a yi musu gwajin, yana mai shawartar ragowar da su ma su bi sahu.
Daga bisani Abubakar Sulaiman ya jagoranci addu’a ta musamman domin neman sauki ga Tukur Ibrahim.
Idan za a iya tunawa, gwamnan jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed da mataimakinsa Sanata Baba Tela sun taba kamuwa da cutar kafin daga bisani gwamnan ya warke.