✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Dan Najeriya ya sanya hannu a kulob din Arsenal

Wani matashin dan kwallo dan asalin Najeriya mai suna Semi Ajayi, ya sanya wa kulob din Arsenal da ke Ingila hannu.Bayanin haka na kunshe ne…

Dan Najeriya Seyi Ajayi da ya sanya hannu a kulob din Arsenal na IngilaWani matashin dan kwallo dan asalin Najeriya mai suna Semi Ajayi, ya sanya wa kulob din Arsenal da ke Ingila hannu.
Bayanin haka na kunshe ne a wata sanarwa da kulob din ya fitar a kafar sadarwarsa a karshen makon jiya.
Bayanin ya ce kulob din ya sayi dan kwallon ne bayan ya haskaka a wasanni biyu a matsayin gwaji da kulob din ya yi masa a kwanakin baya.
Shi dai Ajayi ya taba bugawa kulob din Charlton Athletic kafin kulob din ya raba gari da shi a karshen kakar wasan da ta wuce.
Daga nan ya canza sheka zuwa kulob din Norwich gab da za a fara kakar wasa ta bana daga bisani ya ziyarci kulob din Arsenal a matsayin gwaji.  Wasanni biyu da ya buga a matakin yara a kulob din Arsenal ta sa kulob din ya gamsu da kwazonsa inda ya yanke shawarar dauke shi.
A halin da ake ciki Semi Ajayi, ya sanya hannu a kwantaragin shekara biyu a kulob din na Arsenal sai dai kulob din bai bayyana albashin da dan kwallon zai rika karba ba.
Ajayi ya taba bugawa Najeriya kwallo a matakin yara, don haka zai iya bugawa Ingila kwallo tun da an haife shi ne a garin Crayford na Ingila.
Ajayi, yana wasa ne a bangaren baya (defender).