Gwamnan jihar Gombe, Ibrahim Hassan Dankwambo na jam’iyyar PDP, ya sha kaye a hannun abokin hamayyarsa na jam’iyyar APC, Sanata Ahmad Alkali, a zaben kujerar majalisar dattawan Arewacin Gombe.
Baturen zaben yankin, Farfesa Umar Gurama, ya bayyana cewa Sanata Alkali ya samu kuri’a 152,546 yayin da Gwamna Dankwambo ya samu kuri’a 88016.