Sarkin Fulanin kasuwar shanu da ke Oko-Oba a Jihar Legas, Alhaji Bello danmubaffa ya ce muddin aka ci gaba da takura musu a kasuwar, za su tashi su koma Jihar Ogun, inda suka sayi fili eka 25.
Ya ce ba za su bari ruwan da ya ci abokan zamansu mahauta ya ci su ba, domin baya ga tarin haraji ba a shawarce su ba a yayin da gwamnati ta sayo motocin daukar nama, lamarin da ya sa suka sayi filin, wanda suke sa ran karawa zuwa eka 60.
Sarkin ya ce sun gayyaci sauran ’yan kasuwar su biyo su a duk lokacin da za su yi kaura, kuma za su ba su fili kyauta. “Mun yi ta kokarin a saukake mana yawan takurawa mu da dabbobinmu, ta hanyar kai kukanmu ga gwamnati, amma an yi banza da mu, saboda haka za mu dauki matakin da muke jin ya dace mu”. Inji shi.
Shi ma shugaban Meyetti-Allah na Jihar Legas, Alhaji Abdullahi Laliga ya ce wani abin da ya sa har suka sayi fili a Jihar Ogun shi ne ganin saura wata daya kafin kasuwar ta fita daga hannun Alhaji Idris Yaro Dogara, har mutum 83 sun rubuta wa gwamnatin Jihar Legas suna neman a ba su kasuwar. “Muddin ba a sake mayar wa kamfanin da ke kula da kasuwar ba a halin yanzu, mai yiwuwa a sami matsala, in wanda za a ba bai san harkar dabbobi ba.
Wakilinmu ya yi kokarin jin ta bakin gwamnatin Jihar Legas daga kwamishinan gona, Alhaji Gbolahan Lawal, amma hakan ya ci tura.
Ana dai yanka dabbobi kusan 2,000 a kullum, bayan dimbin jama’a da ke kasuwaci daban-daban a kasuwar.
Dillalan shanu sun yi barazanar barin kasuwar Oko-Oba
Sarkin Fulanin kasuwar shanu da ke Oko-Oba a Jihar Legas, Alhaji Bello danmubaffa ya ce muddin aka ci gaba da takura musu a kasuwar, za…