✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Fadan Kabilanci: Sojoji sun kama mutum 71a Adamawa

Kwamandan Birged din Sojoji na 23, Birgediya Janar Bello Muhammed ya mika mutum 71 da sojoji suka kama kan zargin haddasa fadace-fadacen kabilanci a tsakanin…

Kwamandan Birged din Sojoji na 23, Birgediya Janar Bello Muhammed ya mika mutum 71 da sojoji suka kama kan zargin haddasa fadace-fadacen kabilanci a tsakanin kabilar Waja da Luguda a kananan hukumomin Lamurde da Guyuk na Jihar Adamawa ga ’yan sandan jihar domin gudanar da bincike a kansu.

Janar Muhammad ya ce sun kama mutanen ne bayan sun dauki kwana biyu wajen kawo sulhu a tsakanin kabilun biyu. Ya ce wadannan irin fadace-fadacen kabilanci sun fi shekara 10 ana yin su kuma hakan na kawo barazana ga zaman lafiya da tsaro.

“Wadannan kabilu biyu sun zauna tare da juna tsawon shekaru amma a bara fada ya barke a tsakaninsu har sau uku wadanda suka haddasa asarar rayuka. Amma a fadan da suka yi mun yi nasarar raba fadan sannan mun yi nasarar kama 71 daga cikinsu,” inji shi.

A lokacin da yake mika wadanda ake zargin ga ’yan sandan, Janar Bello ya umarci ’yan sandan su dage wajen gudanar da bincike domin gano ainihin wadanda ke da hannu a haddasa fadace-fadacen. Ya ce dole ne a aiwatar da bincike a tsakanin wadanda aka kame domin mafi yawancinsu matasa ne wadanda suka karya doka.

Mataimakin Kwamishinan ’Yan sanda Mai kula da Harkokin Ta’addanci da Bincike, Abu Bocho, ya ce yana son a samu zaman lafiya a jihar kafin zaben bana, kuma sojoji da ’yan sanda ba za su yi kasa a gwiwa ba wajen kare hakkin dan Adam.