✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Gariyon gogoriyon gwaramar Gwamna gwarangwam

An yi jugun-jugum An yi jimami jim Kui shiru kurum Taraddadin kwaramniya kwararam Gangaren gare-gare gararam Gararambar gwamnoni Gararumar gunguni Gantalin gani-gani Ginsamin gwankin gangamin…

An yi jugun-jugum

An yi jimami jim

Kui shiru kurum

Taraddadin kwaramniya kwararam

Gangaren gare-gare gararam

Gararambar gwamnoni

Gararumar gunguni

Gantalin gani-gani

Ginsamin gwankin gangamin gurnani

Gwangwajewar gwangwani

Girgiza gariyo

Gangin gogoriyo

Gwaramar gangaren gwaranyo

Gwamma an gaurayo

Gagarar gizon gizo-gizo ta lilyo

Ciccike gurbin gwamnoni

Zababbakar zabuka ta zabge

Zuga-zugi sun zuge

Zabarin karon tawadar zuge

Zabi-sonka a Asibicin tuni

Wuraren da akai aringizo

Masu wayo da kwazo

Har sun yi wa mazaje kozo

Wai a ce jagabansu ne gwarzo

A cike gurbi wani zai ci kanzo

Ana ta ganin hazo

Alkaluma na ta gizo

Kuri’u ne bazo-bazo

Takaddama dai ta furzo

Gurmuzu an gurzo

Gwarama

Ganguna gingima -gingima

Garada sun yi gardama

Gundumi mai guduma

Garkar gayaunar garma

Haurobiyawa a hankalta

Lallai a rage shagalta

Kar rigingimu su kazanta

Komai za ai a fahimta

Kar a bi masu karanta

Kundin da-da-na yanzu

Wasu sun fasko tun dazu

Miyagu na ta zazu

’Yan ta-more na wasan karkuzu

Muguwar manufarsu tuni ta bazu

Mu dai yi karatun ta-natsu

Kar mutum ya zama hutsu

Ko a karke da mutsu-mutsu

Ai ta yunkurin tashin tsuntsu

Ana ta tsuwwa tsu-tsu

A daidaita

A saisaita

A sasanta

A karanta

A aikata

Amfanin ilimi

Aiki muhimmi

Ai ta alamta alami

A rika mukamin kaimi

A hana ruwa yai tsami

A daina daukar makami

A watsar da barandami

A kakaba takalmi

A dauki sungumi

A juya akalar rakumi

Asibicin wannan makon ne Hukumar Zabi-sonka ta himmatu wajen karkare zabukan cike gurbin gwaramar gariyon gogoriyon gwamna gwarangwam, a daukacin fadin kasar nan. Kuma za a aiwatar da zabukan ne har a yankunan Arewatawan Haurobiya, wadanda ba su saba da ganin irin wannan gwaramar ba, musamman a birnin Dabo inda ba a dabo; da birnin Shehu Mujadaddi, inda ake ta TATABURZAR TURKA-TURKAR TAMBELEN TUMBIN WULLI. Masu fuka-fukin tashi lallai ku bi dattijai su yi muku karatun KA’IDAR DA KE DAMFARE A KAWA’IDI, tunda kowa ya san sai an bi ka’ida ake samun gwaggwabar fa’ida mai dorewa.

Jaruman jar tagiya sun tamke igiya, a karkashin tutar jam’iyya mai danboto da sanda jirge, suna ta kwankwatsa kwarankwatsin tsiya a GADA-GADAR GUDUN GADAR GUTSURAR GYADAR GUNDUMAR GWARAMAR GANGIN GIRGIZA GARIYON GWAGWAR GWAMNA GARANGWAM. Ban da ARANGAMAR ARTABUN ARINGIZO. Ko dai me aka zabo muna fatan kada a jefa al’umma a cikin jangwam. Ni ba zan ce a zabi wani, a fifita wani a kan wani ba, domin Baban-burin-huriyya ya furta cewa kowane Gwamna gwarangwama da za a gudanar da zabi-sonka na cike gurabu a jiharsa, musamman wadanda ke jan ragama karkashin tutar alamar tsintsiya kowa ya yi ta-kansa.

’Yan makaranta masu koyi-ka-koyar a farfajiyar Dodorido da ke cikin Amintacciyar jaridar kasar Haurobiya, wajibi ne a yi bitar kundin labaran da-da-na yanzu, musamman a wannan zamani namu da aka ce an daina kiwon dabba, mutum ake kiwo. Kun ga ke nan duk wani mai wasan Samson-siya-siya a dama-dama-da-kurda-kurdar siyasar damo-da-kura-diyya da ya fara tara dandazon masu fuka-fukin tashi su yi masa jagwalgwalon jagaliyar jigata al’umma tuni za a fasko manufarsa.

Sannan akwai bukatar a daina GWANGWAJEWAR GWANJON GANYEN GAYE; SUKA-DA-BURTSATSEN MAGANGANU, tare da daukacin al’amuran da ke haifar da karkewa da DAMBARWAR DAMBEN DANDATSAR DAMATSA, sai a yi ta DUMUINIYAR DAGAR DANDAZON DUGUNZUMAR DAMUWA. Mugun kuwa da ya tsara tsuwurwurta tsugudidi da tsangwamar al’umma sai ya arce ya bar su cikin tsomomuwar tsimin tsuma tsumma tsamo-tsamo.

Haurobiyawa mu tunkari tsilli-tsillin matsalolin da ke ci wa al’umma tuwo a akushi, ta yadda za mu fasko ja-gaban al’umma da zai iya jan daga ya yi daga-daga da su. Yin hakan ya zama dole domin kowace al’umma a da can akwai yadda take zaben shugabanta, ta hanyar la’akari da bukatunta a daidai yanayin da ta samu kanta. Wadansu kan zabo MADUGUN FALKE UBAN FATAKE, DON YA FATATTAKI MATSALOLIN CINIKI, wadansu kuwa sukan zabi jarmai don ya ja tungar dagar dagargaza masu kai wa al’umma farmaki bisa zalunci. Uwa-uba akwai wadanda ke fifita zaben Malamin malumma, amma ba malun-malun ba, don ya kawar musu da JUHALA, ya tabbatar da ADALA, ta hanyar karatun ta-natsu, da ke kawar da mutsu-mutsu, tare da hadin gwiwar masu kwazo da suka kasura a fannonin rayuwa, don a fita daga kangin masu rugugin kidan gangin girgiza Gariyon gogoriyon gwaramar Gwamna gwarangwam..

Al’umma A HANKALTA, A SAISAITA, A DAIDAITA, ka da  A SHAGALTA,  ta yadda duk wata JIMURDAR JAN-RAGAMA da ta bijiro, za a iya hana rikidewarta zuwa JAN-RIGIMA ko JUYAYI JUYA AKALAR RAKUMA. Lallai a rage ZALAMA a yi kokarin samun MAKAMA, har al’umma ta daina HAMMA. Kan abin da duk zai tallafa da tarairayar kasar nan sai kowa ya dauki HARAMA.

Baban-burin-huriya da Usainin-Babajo kada ku bari a yi gwanjon alkiblar tunanin Haurobiyawa tamkar yadda su Baba-ojo suka tsiwurwurta suka karbe awalaja, suka yasar da al’umma kowa ya karke da janjanin jaye-jayen ja-in-ja.

Babban batun wannan makaranta dai bai wuce kokarin ganin an karkakare ZABABBAKAR ZABUKAN shekara ta dubu karamin lauje da sili da manuniyar kasa cikin LULLUMIN LUMANA LULLUM!