✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Gwamna Badaru ya nada mataimaka ga matansa 3

Gwamnan jihar Jigawa, Muhammad Badaru Abubakar, ya nada mataimaka na musamman ga matansa uku. A cikin mataimaka 51 da Gwamnan ya nada akwai masu taimaka…

Gwamnan jihar Jigawa, Muhammad Badaru Abubakar, ya nada mataimaka na musamman ga matansa uku. A cikin mataimaka 51 da Gwamnan ya nada akwai masu taimaka masa na musamman akan fitilun hanya da kuma mai lura da adadin jama’a.

Majiyarmu ta samu rahoton cewa, a cikin jadawalin sunayen mataimakan akwai Sa’adatu Bashir Muhammed, mataimakiya ta musamman ga matar Gwamnan ta farko, sannan Mariya Muhammed Muktar mataimakiya ga matar Gwamna ta biyu sai kuma Aisha Garba, Mataimakiya ga matar Gwamnan ta uku.

An bayyana Jadawalin sunayen Mataimakan Gwamnan tare da ayyukan da zasu aiwatar, sai dai kawai na matan Gwamnan ne ba a sanar da ayyukan su ba.