Sakamakon wani gwaji da aka yi ya nuna cewa Gwamnan jihar Bauchi Bala Mohammmed, yana dauke da cutar Coronavirus.
A wata sanarwa da babban mai bai wa gwamnan shawara a kan kafofin yada labarai Mukhtar Gidado ta tabbatar da hakan. Inda ya ce bayan gwajin da Hukumar Yaki da Cututtuka Masu Yaduwa (NCDC) ta yi an tabbatar da mutum shida ne suka kamu da cutar.
A ranar Litinin ne aka shiga zaman zullumi a Bauchi bayan da gwamnan jihar, Bala Mohammed, da kwamishinoninsa guda biyu suka killace kansu sakamakon mu’amala da dan tsohon Mataimakin Shugaban Kasa Atiku Abubakar, wanda aka tabbatar yana dauke da cutar Coronavirus.
Hukumar Yaki da Cututtuka Masu Yaduwa (NCDC) ta sanar da cewa, zuwa yanzu mutum 44 ne suka kamu cutar Coronavirus a Najeriya, mutum 2 sun warke yayin da daya ya rasu, saura mutum 41 da suke da cutar.
2 new cases of #COVID19 have been confirmed in Nigeria: 1 in FCT and 1 in Bauchi
The cases have travel history to Germany and the UK.
As at 06:25 pm on 24th March, there are 44 confirmed cases of #COVID19 in Nigeria. 2 have been discharged with 1 death pic.twitter.com/JbCVwSrxFd
— NCDC (@NCDCgov) March 24, 2020