Kungiyar Gwamnonin APC ta taya Shugaba Kasa Muhammadu Buhari murnar cika shekara 77 a duniya. A ranar Talata ce Shugaban Kungiyar kuma Gwamnan Jihar Kebbi Alhaji Atiku Bagudu, ya aike da sakon a cikin wata sanarwa da ya sanya wa hannu. Ya ce kungiyar tana alfahari da kasancewa tare da Shugaba Buhari wanda ta kira ‘Shugaba abin koyi’ ga dukkan al’ummar wannan zamani.
Gwamna Bagudu ya yi wa Shugaba Buhari godiya kan jajaircewarsa wajen ganin Najeriya ta kai bantenta.
Ya ce “Kungiyar Gwamnonin APC na taya Shugaban Kasa Buhari murnar zagayowar ranar haihuwarsa tare kuma da gode masa kan gudunmawar da yake bayarwa ga kasarmu. Muna matukar alfahari da irin jarumtarsa da adalcinsa wajen tafiyar da mulkin kasar nan. Ka kasance Shugaba abin koyi ga jama’ar wannan zamani kuma muna yi maka fatar alheri.”