An tabbatar da rasuwar mutum biyu a hanyar Legas zuwa Ibadan a jihar Ogun jiya Sallah sanadiyyar hadarin mota. Kwamandan Sashe na Hukumar kare afkuwar hadurra ta Najeriya FRSC na Ogun Mista Clement Oladele, ne ya bayyanawa Kamfanin Dillancin Labarai NAN hakan a Abeokuta babban birnin jihar Ogun a yau Laraba.
Mista Clement, ya ce hadarin farko ya faru ne da misalin karfe 4:52 na asuba a babbar hanyar Legas zuwa Ibadan a kusa da gidan man fetur na AP a garin Shagamu. Ya kuma ce, hadarin ya faru ne tsakanin tirela mai lamba KTU 565 XW inda ta kauce hanya ta yi sanadiyyar aukuwar hadarin.