✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Hadimin Ganduje ya gwangwaje matasa da tallafin Jakuna

Mai bai wa gwamnan jihar Kano shawara kan harkokin matasa, Murtala Gwarmai, ya gwangwaje wani matashi a jihar da tallafin jaki a ranar Alhamis. Gwarmai,…

Mai bai wa gwamnan jihar Kano shawara kan harkokin matasa, Murtala Gwarmai, ya gwangwaje wani matashi a jihar da tallafin jaki a ranar Alhamis.

Matashin da ya amfana da tallafin Jaki daga Mai bai wa gwamna Ganduje shawara, Murtala Gwarmai

Gwarmai, ya rabawa matasan kayan tallafin da suka hada da jaki da babura da kekunan hawa ga wasu marayu da dai sauran su.

Gwarmai, ya rabawa matasan Babura masu kafa biyu da kekunan hawa da kudin naira dubu 100 wasu kuma sun rabauta da bulo 500 da bandiran Kwanan rufi 5 da wani matashi da ya amfana da jaki da dai sauran su.
Matasan da suka amfana da tallafin Babura masu kafa biyu
Marayun da suka amfana da kekunan hawa daga tallafin Gwarmai
Wadan da suka amfana da tallafin Bulo 500 da kwanukan rufi daga tallafin Gwarmai.
Rahotanni sun nuna cewa yayin raba tallafin wanda ya gudana a ma’aikatar matasa da wasanni ta jihar Kano, akalla matasa 40 ne suka amfana da rabon kayan tallafin.
Hadimin ya ce matashin da ya amfana da tallafin jakin, shi ya bukaci a bashi tallafin jakin don ya inganta sana’arsa ta safarar kayan gini da suka hada da Kasa da Yashi da Dutse da Bulo da dai sauransu.
Matasan da suka amfana da tallafin sun bayyana farin cikinsu a fili tare da godewa mai bai wa gwamnan shawara kan harkokin na matasa.